Isa ga babban shafi
Kamaru

An gwabza kazamin rikici a Baminda da ke Kamaru

Akalla mutane biyu aka tabbatar da mutuwar su a rikicin da ya barke tsakanin ‘yan sanda da masu zanga-zanga a yankin masu amfani da harshan Ingilishi na Baminda da ke arewa maso kudancin Kamaru.

Rikicin Baminda ya lakume rayukan mutane 2
Rikicin Baminda ya lakume rayukan mutane 2
Talla

Rahotanni da kafafan yadda labaran talabijin din kasar ke tabbatarwa, ya ce kungiyar matasa yankin ta yi kokarin hana zaman tattaunawar Jami’iyyar PDM, ta shugaba mai ci Paul Piya a Baminda, wanda ya haifar da hargitsin da ‘yansanda sukayi harbi.

Sai dai kakakin jam’iyyar adawa ta SDF, Denis Nkemlemo, ya ce wadanda suka mutu sun kai 4.

Sama da wata guda kenan da kungiyar lauyoyi, malaman makarantu da sauran ma’aikata da ke wannan yanki ke gangami nuna adawa da tauye musu hakokinsu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.