Isa ga babban shafi
Gambia

Gambia ta tsare mutane uku Saboda zargin Shugaba Yahya Jammeh da nuna Kabilanci

A Kasar Gambia jami'an tsaro sun yiwa wasu mutane uku mummunar azaba saboda sun zargi shugaba Yahya Jammeh da fifita kabilar sa kawai amma ba ya kaunar sauran kananan kabilun kasar.

Shugaban kasar Gambia Yahya Jammeh
Shugaban kasar Gambia Yahya Jammeh AFP PHOTO/Don Emmert
Talla

Lauyan mutanen Abdoulie Fatty ya fadi cewa an tsare mutanen uku aka bukaci su sanyan hannu cikin wata takarda inda akayi ta muzguna masu.

Mutanen na iya fuskantar dauri na tsawon shekaru biyu saboda furta cewa Shugaban kasar baya kaunar kabilar Mandigo wadanda yawan su ya kai kashi 41 daga cikin dari na yawan mutan kasar.

Shi kansa shugaban kasar Yahya Jammeh daga kabilar Diola ya fito, wadan da suke cikin kananan kabilun kasar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.