Isa ga babban shafi
Burundi

An soma zaman shawo kan rikicin Burundi

A yau asabbbar an bude taron tattauna samar da sulhu a Burundi, kasar da kwanciyar hankali ya gaggara samuwa tsawon shekara guda, tun lokacin da Shugaba Pierre Nkurunziza ya tsaya takarar shugabanci.

Shugaban kasar Burundi, Pierre Nkurunziza
Shugaban kasar Burundi, Pierre Nkurunziza REUTERS/Evrard Ngendakumana
Talla

Zaman tattaunawa da ake gudanawar a Tanzania, ya samu halarta jami’an gwamantin Burundi, dana Diflomasiya da kuma wakilan kungiyoyin fararan hula.

Sai dai ba a gayyace babban kungiyar adawar kasar ba, a tattaunar da za a kai 24 ga watan Mayu ana gudanar da ita.

Rikicin siyasar Burundi ya lakume rayukan al'ummar kasar da dama tare da tilastawa wasu hijira zuwa kasashen dake makwabtaka da su.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.