Mata 'Yan Kasar Djibouti 9 na Yajin Cin Abinci Saboda Sojan Faransa Sun yi Masu Fyade
Wasu mata tara ‘yan kasar Djibouti dake gudun hijira a Faransa sun shiga rana ta 13 suna yajin kin cin abinci saboda zargin laifukan fyade da sojan Faransa ke yiwa mata dake kasar su.
Wallafawa ranar:
Matan sun ki cin abinci sai dai kawai ruwa, da shayi suke ta sha tun lokacin da suka fara yajin kin cin abinci.
Mata ‘yan kasar Djibouti 10 suka shiga wannan yajin kin cin abinci a Paris amma daya daga cikin su ta jingine yajin ranar Juma’a data gabata.
Matan na kwance ne a bisa kananan gado da suna baza a wani yanki dake kudancin Paris.
Hudu daga cikin matan sun bayyana cewa sojan Faransa sun yi masu fyade a lokacin da suka tafi kasar su aiki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu