Isa ga babban shafi
Djibouti- France

Mata 'Yan Kasar Djibouti 9 na Yajin Cin Abinci Saboda Sojan Faransa Sun yi Masu Fyade

Wasu mata tara ‘yan kasar Djibouti dake gudun hijira a Faransa sun shiga rana ta 13 suna yajin kin cin abinci saboda zargin laifukan fyade da sojan Faransa ke yiwa mata dake kasar su.

Shugaban kasar Djibouti Ismail Omar Guelleh  a wani taro a Addis-Abeba.
Shugaban kasar Djibouti Ismail Omar Guelleh a wani taro a Addis-Abeba. REUTERS/Tiksa Negeri
Talla

Matan sun ki cin abinci sai dai kawai ruwa, da shayi suke ta sha tun lokacin da suka fara yajin kin cin abinci.

Mata ‘yan kasar Djibouti 10 suka shiga wannan yajin kin cin abinci a Paris amma daya daga cikin su ta jingine yajin ranar Juma’a data gabata.

Matan na kwance ne a bisa kananan gado da suna baza a wani yanki dake kudancin Paris.

Hudu daga cikin matan sun bayyana cewa sojan Faransa sun yi masu fyade a lokacin da suka tafi kasar su aiki.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.