Isa ga babban shafi
Masar

Ministan shari’ar Masar Ahmed al-Zind ya shiga tsaka mai wuya

Yanzu haka ministan shari’ar kasar Masar Ahmed al-Zind ya shiga tsaka mai wuya sakamakon kalaman da ya yi wanda al’ummar Musulmin kasar ke kallon sa a matsayin cin zarafin Manzan Allah (SAW).

Ministan shari'ar Masar Ahmed al-Zind
Ministan shari'ar Masar Ahmed al-Zind Reuters
Talla

Tuni Gwamnatin Masar ta kori Ministan shari’ar kasar saboda  katobarar da yayi na cewar ko Manzan Allah wanda tsira da amincin Allah suka tabbata a gare shi ne yayi masa kazafi zai sa a kama shi a hira sa da tashar talabijin din Sada al Balad.

Ministan yayi katobarar ce wajen mayar da martani  kan kama wani Dan Jarida saboda zargin cewar ya bata masa suna.Sai dai kafin kammala shirin, ministan ya nemi ahuwa, inda ya ce subutar baki ne, amma hakan bai sa ya tsira ba daga suka daga dubban mutane.

Ita ma Jami’ar Al Azhar ta yi gargadi a kai, inda ta bukaci mutunta Manzan Allah (SAW), yayin da kungiyar kare Hakkin Bil Adama ta Human Rights watch ta ce irin wadannan kalamai na haifar da tashin hankali.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.