Isa ga babban shafi
Central Africa

Farfesa Faustin-Archange ya zama Shugaban Kasar Janhuriyar Africa

Al'ummar kasar Janhuriyar Tsakiyar Africa sun sami sabon Shugaban kasa bayan babban zaben kasar da akayi ba dadewa.Sabon Shugaban kasar Shine Faustin-Archange Touadera,mai shekaru 58, tsohon Fira Minista  kuma Malamin darasin lissafi, wanda ya tsaya a matsayin dan takara na indifenda. 

Sabon Shugaban kasar Janhuriyar Tsakiyar Africa Faustin-Archange Touadéra
Sabon Shugaban kasar Janhuriyar Tsakiyar Africa Faustin-Archange Touadéra (Photo : AFP)
Talla

Hukumar zaben kasar ta sanar da cewa ya sami kashi sittin da biyu daga cikin dari na yawan kuri'u da aka jefa.

Mai bi masa shine Anicet-George Dologuele wani tsohon ma'aikacin Banki wanda ya sami yawan kuri'u kashi 37 daga cikin dari na yawan kuri'u da aka jefa.

A zagayen farko ya baiwa mutan kasar mamaki kasancewar shine yazo na biyu a zaben.

Ya kasance mutan kasar na matukar girmamashi a matsayin malamin darasin lissafi wanda yayi karatu har ya zama Farfesa.

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.