Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

Mutanen Sudan ta kudu na mutuwa saboda Yunwa

Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya yace dubban mutane na rasa rayukansu sakamakon masifar yunwa a kasar Sudan ta Kudu, yankin da ake tafka yaki, tsakanin dakarun gwamnati da na ‘yan tawaye.

Dubabban mutane suka gujewa gidajensu saboda rikici tsakani tsakanin dakarun gwamnati da na 'Yan tawaye a sudan ta Kudu
Dubabban mutane suka gujewa gidajensu saboda rikici tsakani tsakanin dakarun gwamnati da na 'Yan tawaye a sudan ta Kudu REUTERS/James Akena
Talla

Majalisar Dinkin Duniya ta roki bangarorin da ke rikici su su bari a shigar da kayan jinkai ga mabukata

Rahoton yace mabukata abinci cikin gaggawa sun kai dubu arba’in don lamarin ya kai inda ya kai.

A cewar rahoton lamarin na kara muni kullum domin kashi dubban mutanen kasar na cikin mawuyacin hali.

A 2013 ne rikici ya barke a Sudan ta kudu bayan shugaban kasar Salva Kiir ya zargi tsohon mataimakinsa Reik Machar da yunkurin kifar da gwamnatinsa.

Tun a lokacin dakarun da ke biyayya ga shugabannin biyu ke gwabza fada.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.