Boko Haram
Sojoji sun kashe ‘Yan Boko Haram 12
Sojojin Najeriya sun kashe ‘Yan Boko Haram 12 tare da kwato makamai da dama daga hannun Mayakan a yankin Damboa cikin Jihar Borno arewa maso gabashin kasar.
Wallafawa ranar:
Talla
A cikin wata sanarwa, kakakin rundunar Sojin Najeriya Kanal Sani Usman Kukasheka ya ce jami’an Sojinsu sun kashe mayakan ne a lokacin da suke gudanar da aiki tsakanin sabon gari zuwa Damboa.
Kuma cikin mayakan da aka kashe har da shugabansu Ameer a Bulagaya. Sannan a ranar lahadi sojojin sun kashe ‘yan boko haram 9 a kauyen Mainari.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu