Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

Sama da mutane dubu 2 ke gudun hijira daga Afrika ta Tsakiya

A wani Rahota da ta fitar Majalisar Dinkin Duniya ta ce sama da 'yan gudun hijira 2000 suka tserewa rikicin Afrika ta Tsakiya zuwa Jamhuriyar Demokradiyar Congo a makon da ya gabata.

Shugabar Rikwan Kwarya a Afrika ta Tsakiya Catherine Samba-Panza
Shugabar Rikwan Kwarya a Afrika ta Tsakiya Catherine Samba-Panza AFP PHOTO / TIMOTHY A. CLARY
Talla

Shugaban hukumar 'yan gudun hijira ta Majalisar Antonio Guiterres ya bayana cewa mutanen sun isa yankunan arewa maso gabacin Jamhuriyar Demokradiyar Congo a cikin hali na tagayara.

Shugaban ya kuma soki hukumomin Jamhuriyar Demokradiyar Congo kan yadda suka umurci jami’an tsaro da su rufe kan iyakar kasar da Afrika ta tsakiya.

Tun lokacin da rikici Afrika ta Tsakiya ya barke kasashen dake makwabtaka da su, suka fara rufe iyakokinsu domin kaucewa kutse 'yan gudun hijira.

Shugaban Rikwan kwaryar kasar Catherina Samba Panza da a yanzu ta Umarce zaman makoki a kasar na kwananki uku sakamakon mutuwar mutane da dama a rikici, na ci gaba da kokarin shawo kan rikicin kasar domin samar zaman lafiya.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.