Isa ga babban shafi
Cote d'Ivoire

ICC ta yi watsi da bukatar bayar da belin Gbagbo

Alkalan Kotun ICC da ke hukuntan laifukan yaki sun yi watsi da bukatar sakin tsohon shugaban Cote d’Ivoire Laurent Gbagbo na wuccin gadi saboda dalilai na rashin lafiya.

Tsohon Shugaban Cote d'Ivoire Laurent Gbagbo
Tsohon Shugaban Cote d'Ivoire Laurent Gbagbo AFP PHOTO/ POOL/ MICHAEL KOOREN
Talla

A watan Nuwamba ne kotun za ta fara sauraren karar Gbagbo wanda ake tuhuma da jefa Cote d’Ivoire cikin yakin basasa a lokacin da ya ki sauka kan madafan ikon kasar bayan ya sha kaye a zaben shugaban kasa da aka gudanar 2010.

Gbagbo na fuskantar tuhume tuhume guda hudu da suka kunshi cin zarafin bil’adama.

Mutane sama da 3,000 suka mutu a rikicin Cote d’Ivoire da aka shafe watanni ana gwabza fada tsakanin dakarun da ke biyayya ga Gbagbo da kuma wadanda ke biyayya ga shugaba na yanzu Alassane Ouatarra.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.