Isa ga babban shafi
Sudan ta kudu

Majalisar dinkin duniya ta yiwa Sudan ta kudu gargadin karshe

Kwamitin Sulhu na Majalisar dinkin duniya ya gargadi Gwamnatin Sudan ta kude cewa zai dauki mataki mai tsauri a kan ta muddin ta ki sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiyar kasar a wannan larabar.

Shugaban kasar Sudan Salva Kiir da Jagoran 'yan tawayen Riek Machar
Shugaban kasar Sudan Salva Kiir da Jagoran 'yan tawayen Riek Machar
Talla

Shugabar kwamitin kuma Jakadiyar Najeriya a Majalisar, Amsada Joy Ogwu ta bayyana matsayin daukacin kasashen da ke Majalisar na tabbatar da cewar Shugaba Salva Kiir ya sanya hannu kan yarjejeniyar kamar yadda ya yi alkawari.

Kara wasti da batun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya zai sanya majalisar kakabawa gwamnatin Sudan ta kudu takunkumi.

A na dai saran shugabanin kasashen Kenya, Uganda, Sudan da Habasha su halarci zaman sanya hannun.

Akalla kashe 70 ciki 100 na al’ummar sudan ta kudu ne ke fama da rashin abinci, yayin da sama da fararan hula dubu 200 ke mafaka a sansani dakarun Majalisar dinkin duniya sakamakon rikicin kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.