An hallaka tsohon Shugaban Soji a Burundi
Wani dan bindiga ya harbe tsohon shugaban Soji a Burundi wanda ya jagoranci kasar a lokacin yakin basasa kasar na tsawon shekaru 13. Kamar dai ya da iyalansa suka shaidawa kamfanin dilanci labaran Faransa.
Wallafawa ranar:
Kanal Jean Bikomagu tsohon babban jigo dakarun Tutsi ne da suka fafata a kasar, kuma Maharin ya harbe shi ne a cikin motar sa a dai-dai loakcin da ya ke kokarin shiga gidansa a Kinindo da ke yammacin birnin Bujumbura.
Har yanzu dai ba a tantace wanda ya kai masa hari ba.
Sai dai kuma harin na zuwa ne kasa da makonin biyu bayan kashe tsohon kwamanda askarawa kasar Janar Adolphe Nshi-miri-mana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu