Tanzania
MDD ta bukaci Tanzania ta kwantar da hankali kan Ebola
Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci al’ummar kasar Tanzania su kwantar da hankalinsu sakamakon rasuwar wani dan gudun hijira da ya zubar da jini ta ido da kunne kafin ya mutu wanda ake cewa cutar ebola ce.
Wallafawa ranar:
Talla
Hukumar lafiya ta Majalisar da kuma hukumar kula da Yan gudun hijira sun ce binciken da jami’ai suka gudanar bai nuna musu cewar cutar ebola ce ta kashe mutumin ba.
Mai Magana da yawun ma’aikatar lafiyar kasar Nsachiris Mwamwaja yace ana cigaba da gudanar da binciken likita akan gawar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu