Boko Haram ta kai jerin hare hare a N'djamena da Maiduguri
Mutane 14 ne suka rasa rayukansu a wani harin kunar bakin wake da aka kai wajen hada-hada kasuwanci Jama’a a cikin birnin N’djamena na kasar Chadi, kwanaki kalilan bayan mayakan Boko haram sun dau alhakin kai harin baya da ya yi ajali mutane 38 a kasar.
Wallafawa ranar:
Rahotanin sun ce maharin ya yi shiga ne irin ta mata tare da tarwatsa kansa a tsakiyar kasuwa.
Wannan kuma dai na zuwa ne a dai-dai lokaci da wasu rahotanin ke tabbatar da kai hari a tashar mota da ke garin Maiduguri na jihar Borno a safiyar yau wanda mutane 2 suka rasa rayukansu.
Ko a daran Jiya sai da aka kai hari a kauyen Ngamdu mai nisan Kilometer 100 da maiduguri inda mutane 11 suka mutu.
Kamfanin dilanci Labaran Faransa AFP ya rawaito cewa a ‘yan tsaka-kaninan mutane akalla 580 ne suka rasa rayukansu a jerin hare hare Boko Haram.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu