Isa ga babban shafi
Burundi-MDD

Majalisar dinkin duniya ta gargadi shugaban Nkurunziza kan aniyarsa

Shugaban Kasar Burundi Pierre Nkurunziza ya yi watsi da barazanar da Majalisar Dinkin Duniya ta yi na sanyawa kasar takunkumi kan shirin sa na neman wa’adi na uku, inda yace babu gudu babu ja da baya.

Shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza
Shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza REUTERS/Jean Pierre Aime Harerimana
Talla

Mai Magana da yawun shugaban Philippe Nzobonariba ya shaidawa al’ummar kasar cewa, babu abinda zai hana takarar shugaban, wanda tuni hukumar zabe ta sanya 15 ga watan gobe a matsayin ranar gudanar da zaben.

Kwamishinan jin kai na Majalisar dinkin Duniya Zeid Raad Al Hussein yace, tashin hankalin da ake samu na iya haifar da yakin basasa a kasar inda ya yi kira da bangarorin biyu bisa yin la’akari da halin da suke kokarin jefa kasar a ciki .
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.