Uganda
‘Yan tawayen Uganda sun fille kan mutane 5
Hukumomin Kasar Jamhuriyar Demokuradiyar Congo sun ce ‘Yan Tawayen Uganda sun fille kan wasu ‘yan kasar 5 a garin Mbau. Shugaban mazauna Yankin, Amisi Kalonda ya ce an kashe mutanen ne da safe lokacin da suke tafiya wurin aiki. Jami’in yace an shaidawa sojoji harin, amma kafin su kai dauki maharani sun gudu.
Wallafawa ranar:
Talla
Garin Mbau na kusa ne da Beni gari mafi girma a lardin Nord Kivu.
Mahukuntan Uganda kuma sun daura alhakin kai harin ne akan ‘Yan tawayen Uganda wadanda suka kashe mutane sama da 260 a karshen shekarar da ta gabata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu