Isa ga babban shafi
Boko Haram

An kafa gidauniya ga iyalan Sojojin Nijar

An kaddamar da wata gidauniya a Jamhuriyyar Nijar domin tara kudaden da za a taimaka wa iyalan sojojin kasar Nijar da ke yakar Boko Haram na Najeriya. Kungiyoyin ‘yan jarida na kasar ne suka bayar da shawarar kafa gidauniyar.

Zanga-zangar adawa da Boko Haram a Yamai
Zanga-zangar adawa da Boko Haram a Yamai AFP/Boureima Hama
Talla

Ministan yada labaran Nijar Yahuza Sadisu Madobi ya ce zuwa yanzu an tara kudaden da yawansu ya kai CFA bilyan biyu.

A makon da ya gabata dubban mutanen Nijar sun fito suna zanga-zangar nuna goyon baya ga dakarun Nijar domin ba su kwarin gwuiwa ga yakin da suke yi da Mayakan Boko Haram da ke barazana ga zaman lafiya a kasar.

Ana sa ran Shugaban kasar Togo Faure Gnassingbé da takwaransa na Benin Thomas Yaya Boni za su kai ziyara kasar Nijar domin tattaunawa da Shugaba Mahammadou Issoufou game da barazanar Boko Haram.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.