Isa ga babban shafi
Sudan

Sudan ta kwace Jaridu 13

Jami’an tsaro a Sudan sun yi wa wasu kamfanonin Jaridun kasar dirar mikiya inda suka kwace kwafin jaridu 13 da aka buga a yau Litinin. Babu kuma wani dalilin kwace Jaridun da Jami’an tsaron suka bayar kamar yadda rahotanni suka tabbatar.

Shugaban Sudan Omar Hassan Al Bashir
Shugaban Sudan Omar Hassan Al Bashir
Talla

‘Yan jarida da ke aikin yada labaran keta hakkin bil’adama a Sudan sun ce gwamnatin kasar ta dade tana kwace kwafin jaridu da suka buga labarin da ya saba wa ra’ayinta.

Editan Jaridar Al-Tayar, Osman Mirghani ya shaidawa kamfanin dillacin labaran Faransa cewa Jami’an tsaro sun kwace kwafin jaridarsa ba tare da wani dalili ba.

Sauran Jaridun da aka kwace sun hada da Al-Rai al-Aam da Al-Intibaha da Akhir Lahza da Al-Ahram al-Youm da Awal al-Nahar da Al-Watan da Al-Sudani da Alwan, Al-Saiha da Al-Mijhar al-Siyasi da Al-Dar da kuma Hikayat.

Sudan dai na cikin kasashen da ke sahun gaba a rahoton Kungiyar Reporters without Borders wajen kuntatawa ‘yancin jarida a duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.