Isa ga babban shafi
Ebola

An bude sabuwar makabartar Ebola a Liberia

Gwamnatin kasar Liberia ta bude sabuwar Makabarta ta musamman domin Jana’izar mamatan cutar Ebola a birnin Monrovia. Wannan na cikin matakan da gwamnatin kasar ta dauka domin dakile yaduwar cutar da ke kisa cikin hanzari.

Jami'an kiwon lafiya suna kokarin kawar da gawawwakin mutanen da suka mutu sakamakon Ebola a Liberia
Jami'an kiwon lafiya suna kokarin kawar da gawawwakin mutanen da suka mutu sakamakon Ebola a Liberia John Moore/Getty Images
Talla

Hukumar Lafiya ta duniya WHO ta fitar da sabon alkaluman mamata sakamakon cutar Ebola a yammacin Afrika, inda ta ke cewa mamata sakamakon cutar sun kai 7,842.

Mamatan na daga cikin mutane sama da dubu 20 da aka gwada suna da cutar a kasashen Guinea da Liberia da Saliyo.

Hukumar tace baya ga wadannan kasashe an kuma samu mamata shida a kasar Mali, guda a Amurka sannan kuma 8 a Najeriya.

A kasar Liberia, mutane kimanin 3,500 suka mutu sakamakon Ebola.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.