An kai wa mabiya Shi’a harin bom a Potiskum
Akalla mutane 15 suka mutu a wani harin kunar bakin wake da aka kai wa mabiya Shi’a a garin Potiskum Jihar yobe a Najeriya. harin kuma ya jikkata mutane sama da 50, kamar yadda wani shugabannin mabiya Shi’a a yankin ya tabbatar. Malamin yace an kai wa mabiyansu hari ne a yayin da suke gudanar da bikin Ashura a garin Potiskum.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kuma yace an samu mutuwar mutane 15 ne bayan da Sojoji suka bude wuta da zuwansu inda aka kai harin. Zuwa yanzu babu wani bayani daga Sojojin na Najeriya game da faruwar al’amarin.
Wani shedun gani da ido da wakilin RFI a Yobe ya zanta da shi yace Maharin ya shiga cikin jerin mabiya Shi'a ne a lokacin da suke Mazahara kafin ya dalawa kansa Bom. nan take ne kuma aka samu gawawwakin mutane zube a kasa.
Rahoto: An kai wa mabiya Shi’a harin bom a Potiskum
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu