Isa ga babban shafi
Najeriya

Mutane 21 suka mutu a harin Abuja

Akalla mutane 21 aka ruwaito sun mutu a wani harin bom da aka kai a wata cibiyar hada hadar kasuwanci a birnin Abuja, al’amarin da ya jikkata mutane kimanin 17. An kai harin ne a shagunan Emab Plaza a dai dai lokacin da Najeriya ke shirin fafatawa da Argentina a gasar cin kofin duniya a kasar Brazil.

Harin Bom da aka kai a shagunan Emab Plaza a Abuja.
Harin Bom da aka kai a shagunan Emab Plaza a Abuja. AP
Talla

Kakakin ‘Yan sanda Frank Mba yace zuwa yanzu mutane 21 suka tabbatar da mutuwarsu, 17 suka jikkata. Akwai wani da ‘Yan sanda suka cafke wanda ake zargin yana cikin wadanda suka kai harin tare da bindige dan uwansa.

Emab Plaza, da ke yankin Wuse 11 wuri ne da ke hada cunkoson Jam’a kusa da Masallacin Juma’a kuma rahotanni sun ce kimanin motoci 40 ne suka kone.

Cikin wadanda suka mutu akwai Malam Suleiman Bisallah tsohon mataimakin editan Jaridar Daily Trust da ke aiki da sabuwar Jaridar New Telegraph.

01:20

Rahoton Aminu Manu daga Abuja

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.