Isa ga babban shafi
ECOWAS

Taron shugabannin ECOWAS a Ghana

Shubannin Kasashen yammacin Afrika zasu yi wani taro gaggawa a kasar Ghana, karkashin kungiyar hadin kan yankin, ta ECOWAS ko CEDEAO, domin tattauna matsalar tsaron Yankunansu musamman barazanar ayyukan ta’addanci a Mali da Najeriya.

Shugaban Cote d'IVoire Alassane Ouattara kuma shugaban ECOWAS a lokacin da yake ganawa da Goodluck Jonathan na Najeriya a filin saukar jirgi na Felix Houphouet Boigny a Abidjan
Shugaban Cote d'IVoire Alassane Ouattara kuma shugaban ECOWAS a lokacin da yake ganawa da Goodluck Jonathan na Najeriya a filin saukar jirgi na Felix Houphouet Boigny a Abidjan REUTERS/Luc Gnago
Talla

Wannan shi ne karon farko da shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama zai karbi bakuncin taron, tun lakacin da aka zabe shi shugaban Majalisar shugabannin na ECOWAS a watan Fabrairun bana.

A Shekarar 2012 kasar Mali ta tsunduma cikin rikici, lokacin da ‘Yan tawayen Abzinawa, suka tayar da kayar baya a arewacin kasar, yayin da kuma hankulan duniya suka koma Najeriya, bayan da Mayakan kungiyar Boko Haram sun yi awon gaba da wasu ‘yan mata sama da 200 a watan Afrilu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.