Hukumar SSS ta sake kwacewa Sanusi Lamido Fasfo
Tsohon Babban gwamnan Bankin Tarayyar Najeriya wanda aka tube a cikin watan Fabarairun da ya gabata Sanusi Lamido Sanusi, ya zargin shugaban kasar Goodluck Jonathan da bai wa ‘yan sanda umurnin sake kwace masa Passport a cikin daren jiya, lokacin da ya je filin jiragen sama na Kano domin yin balaguro zuwa kasashen waje.
Wallafawa ranar:
Sanusi, wanda ke zantawa da manema labarai yau lahadi a birnin Kano, ya ce ‘yan sandan farin kaya wato SSS, sun sake karbe masa Passport wanda kotun ta bayar da umurnin a mayar masa, yayin da ‘yan sandan ke ci gaba da rike Passport dinsa na diflomasiyya.
An dai tube Sanusi Lamido Sanusi daga kan mukaminsa ne bayan da ya yi zargin bacewar wasu bilyoyin kudade a kamfanin hada-hadar man fetur na kasar wato NNPC.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu