Najeriya
‘Yan bindiga sun hallaka mutane 38 a Jihar Bornon Najeriya
Rahotanni daga Najeriya sun ce, wasu ‘Yan bindiga sun hallaka mutane 38 a Jihar Borno da suka hada da makiyaya da kuma ‘Yan aikin sa kai.
Wallafawa ranar:
Talla
Wakilin wani kauye a Jihar Borno, Alhaji Garba Ali ya ce ‘yan bindigan sun kashe makiyaya 14 a kauyansu, yayin da kuma wasu sanye da kayan soji suka kashe ‘Yan banga 24 a wani daji dake Jihar.
Kamfanin dillancin labaran Faransa ya ruwaito cewar, yan bindigan sanye da kayan sarki sun yaudari ‘Yan bangan inda suka kaisu daji yayin da suka kashe 24 daga cikin su, kana 34 suka bata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu