Isa ga babban shafi
Zimbabwe

Kotun kolin Zimbabwe ta amince da sakamakon zaben kasar

Kotun Kolin kasar Zimbabwe, ta amince da cewar, shugaba Robert Mugabe ne ya lashe zaben shugaban kasar da aka yi a karshen watan da ya gabata.

Shugaban kasar Zimbabwe, Robert Mugabe
Shugaban kasar Zimbabwe, Robert Mugabe REUTERS/Siphiwe Sibeko
Talla

Mai shari’a Godfrey Chidyausiku, ya bayyana cewar an gudanar da zaben ne ba tare da wani magudi ba, hukuncin da yanzu ya bada damar rantsar da shugaban a wa’adi na bakwai.

A karshen makon day a gabata kungiyar kasashen kudancin Afrika ta SADC ta amince da sakamakon zaben kasar, inda ta nada Mugabe a matsayin mataimakin shugabar kungiyar.

Jam’iyar adawa ta MDC na ikrarin zaben na tattare da magudi da dama inda ta janye wata kara da ta shigar a gaban kotu tana mai ikrarin cewa ba za a musu adalci ba.

A wannan makon ne ake sa ran za a rantsar da shugaba Mugabe, dan shekaru 89 a wa’adi na bakwai inda zai sake kwashe shekaru biyar yana mulki.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.