Isa ga babban shafi
DRC Congo

Ntaganda ya gurfana a gaban kotun manyan laifuka ta duniya

Madugun ‘Yan-tawayen kasar Jamhuriyar Demokardiyar Congo, Bosco Ntanganda, da ake zargi da hannu wajen laifukan yaki, yanzu haka na gaban Kotun kasa-da-kasa da ke Hague domin sauraron irin hukuncin da za a yi masa.Ntanganda wanda a tarihin kotun shine na farko da ya mika kansa gaban kotun da ta dade tana cigiyarsa, ya kwana tsare hannun kotun ne, bayan ya mika kansa.  

Shugaban 'Yan tawayen kasar Jamhuriyar Demokradiyar Congo, Bosco Ntaganda
Shugaban 'Yan tawayen kasar Jamhuriyar Demokradiyar Congo, Bosco Ntaganda REUTERS/Paul Harera
Talla

Ntanganda wanda akewa lakabi da “Terminator” tun ranar Litini wancan makon ya kai kansa ofishin jakadancin Amurka dake Rwanda, inda ya nemi su kaishi Kotun kasa-da-kasa dake Hague.

Yanzu haka dai yana tsare a hannun kotun dake Hague.

Ana zarginsa ne da yin sanadin kisan mutane akalla 800 mazauna kauyuka a kasar ta Congo, sannan kuma ya rika diban ‘yan kana nan yara aikin soja, da gallazawa mata , duk a tsakanin 2002-2003.

Ya kasance na biyar dan Afrika dake gaban wannan kotun, da za ta fara sauraron laifinsa.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.