Isa ga babban shafi
Mali

An wawushe dukiyar Larabawa da Abzinawa a Gao bayan ficewar ‘Yan tawayen Mali

Babu abinda ya rage a shagunan Tsirarun Larabawa da ke kasuwanci a birnin Gao bayan wasu mazauna garin sun wawushe dukiyarsu saboda zargin suna taimakawa Mayakan Ansar Dine da suka karbe ikon Yankin Arewacin Mali tsawon watanni Tara.

Filin Jirgin birnin Gao
Filin Jirgin birnin Gao AFP PHOTO / ROMARIC OLLO HIEN
Talla

Tun bayan da Dakarun Faransa da Mali suka karbe ikon Gao daga Mayakan Mali, Larabawa da Abzinawa ke fuskantar fashi daga matasan garin.

Tuni Larabwa suka fice daga Gao domin tsira da rayuwarsu.

Nisan Kilomita 1,200 ne tsakanin Gao zuwa Bamako babban birnin kasar Mali. Kuma Rahotanni sun ce kimanin mutane 350,000 suka fice bayan ‘Yan tawaye sun karbe ikon garin.

Tun a farko Faransa da Amurka da Tarayyar Turai suka yi gargadin za'a iya kai hare haren ramuwar gayya ga tsirarun Larabwa da abzinawa idan aka karbe ikon biranen Gao da Timbuktu da Kidal.

 

Majalisar Dinkin Duniya ta fara shirye shiryen aikawa da Dakaru domin karbe ragamar tafiyar da tsaro daga hannun dakarun Faransa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.