Isa ga babban shafi
Zimbabwe

Mugabe ya yi Allah wadai da NATO saboda kifar da gwamnatin Ghaddafi

Shugaban Kasar Zimbabwe, Robert Mugabe, ya zargi kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da mallakar akidar yaki, yayin da yayi Allah wadai da yadda kungiyar NATO ta kifar da gwamnatin shugaba Muammar Ghaddafi a Libya.

Shugaban kasar Zimbabwe, Robert Mugabe
Shugaban kasar Zimbabwe, Robert Mugabe
Talla

Yayin da yake jawabi a Majalisar Dinkin Duniya, shugaba Mugabe, ya zargi kasashen NATO da girman kan da suke ganin cewar sun fi karfin kowa a duniya, inda sukayi watsi da daukacin shirin kungiyar kasashen Afrika na sasanta rikicin Libya.

Sai dai yai kiran kawo karshen yadda manyan kasashen duniya ke yin gaban kansu, wajen murkushe abokan gabansu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.