Libya
Mustapha Abduljalil na kasar Libya ya gargadi masu yunkurin raba kasar gida 2
Shugaban gwamnatin rikon kwaryar kasar Libiya Mustapha Abduljalil, ya yi barazanar maida raddi ta karfi wajen hana duk wani yunkurin balle yankin gabashin kasar, da wasu dakarun sa kai ke yi.A cikin wani jawabi da aka yada ta kafar Talabijin din gwamnatin kasar, Mustapha Abduljalil ya bayyana cewa, ba a shirya raba kasar Libiya ba.tare da yin kira ga yan uwansa da ke yankin, da su rungumi hanyar tattaunawa, su kuma daina biye wa tsohin aminan Kanal Kaddafi, wadanda yace za su yi iya yinsu wajen ganin sun kare da su
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: