Isa ga babban shafi
Najeriya

Shugaban Najeriya yace an cafke wasu da ake zargin sun kai hari a Kano

Shugaban Najeriaya Goodluck Jonathan yace an cafke wasu da ake zargin sun kai hari a birnin Kano wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane 178, tare da jaddada ci gaba da farautar ‘Yan kungiyar Boko Haram.A cewar shugaban Jonathan akwai wasu dake daukar nauyin su, domin a ko ina a duniya akwai wasu da ke daukar nauyin aikin ta’addanci.

Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan tare da Sarkin Kano Ado Bayero, a lokacin da ya kai ziyara garin Kano
Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan tare da Sarkin Kano Ado Bayero, a lokacin da ya kai ziyara garin Kano REUTERS/Stringer
Talla

Ziyarar shugaban na zuwa ne kwanaki biyu bayan wata musayar albarussai da harin bom da aka kai a birnin Kano bayan kammala sallar Juma’a.

Tun fara mulkin Jonathan a Najeriya yake fuskantar kalubale da rikicin Boko Haram wanda ke kokarin jefa kasar cikin yakin basasa.

Shugaba Jonathan ya kai ziyara wuraren da aka kai hare haren da kungiyar boko Haram ta yi ikirarin daukar nauyi da suka hada da hedikwatar ‘Yan sanda.

Shugaban ya gana da Sarkin Kano mai Martaba Ado Bayero, inda yake cewa aikin ta’addanci ga wani mutum daya ya shafi al’umma baki daya.

Bayan kai harin Bom a garin kano an sake samun rikici a bangaren Arewacin Najeriya, inda mutane 10 suka mutu bayan musayar wuta a garin Tafawa Balewa a Jahar Bauchi.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.