Rwanda
Kagame ya yi na’am da kiran yin tazarce
Shugaban Kasar Rwanda, Paul Kagame, yace ba shi da wata matsala ko kadan, da masu kiran sauya kundin tsarin mulkin kasar, don bashi damar yin tazarce a karo na uku.
Wallafawa ranar:
Talla
Yayin da yake ganawa da manema labarai a Uganda, shugaba Kagame yace, kowa na da damar fadin albarkacin bakinsa, kuma shi bashi da hurumin hana ‘Yan kasar abinda suke so.
Rahotanni sun ruwaito Ministan tsaron cikin gida, Sheikh Fazil Musa Harerimana na bukatar ganin an sauya kundin don bai wa Kagame damar ci gaba da mulki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu