Isa ga babban shafi
Tunisiya

Jam’iyyar Musulunci ke kan gaba a zaben Tunisiya

Jam’iyyar musulunci ta Ennahda ta yi ikirarin lashe zaben farko na ‘yan majalisu da aka gudanar tun bayan hambarar da gwamnatin Zine Al Abidine Ben Ali.A yau ne ake sa ran bayyana sakamakon zaben amma Jam’iyyar Ennahda ta bayyana samun nasarar zaben bisa bayanan da ta tattara a runfunan zabe.Yanzu haka kuma magoya bayan Jam’iyyar sun barke da kabbara tare da rera taken Tunisia bayan da shugaban yakin neman zaben jam’iyyar Abdulhamid Jlazzi ya bayyana jam’iyyar Ennahda ce akan gaba.An samu fitowar masu kada kuri’a da kusan kashi 90 domin zaben ‘yan majalisun da zasu sake fasalta kundin tsarin mulkin kasar da zai bada damar zaben sabuwar gwamnati a shekarar 2013 

Rached Ghannouchi Shugaban Jam'iyyar ta Ennahda a wani gangami da Jam'iyyar ta hada, à Tunis
Rached Ghannouchi Shugaban Jam'iyyar ta Ennahda a wani gangami da Jam'iyyar ta hada, à Tunis AFP/FETHI BELAID
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.