Tunisiya
Gwamnatin Tunisya ta za ayi zabuka a watan Yuli
Gwamnatin rikon kwaryar kasar Tunisya ta bayyana shirin gudanar da zabuka cikin watan Yuli, kamar yadda aka tsara.PM Beji Caid Essebsi ya tabbatar da haka, kuma a makon jiya shi ne ya nuna nuna shakku kan yuwuwar gudanar da zabukan. Wannan bayan kawar da gwamnati Zine el-Abidine Ben Ali cikin boyen juyin juya hali.Yayin ziraya zuwa birnin Paris na kasar Faransa, PM Essebsi ya shaida wa wani gidan rediyo cewa tun ranar da suka shiga cikin gwamnati suke kokarin tabbatar da ganin an yi zabe ranar 24 ga watan Yuli, kamar yadda aka tsara.Bayan ban kwana da madafun ikon kasar ta Tunisiya, Ben Ali ke zaman gudun hijira a kasar Saudiya.
Wallafawa ranar: