Isa ga babban shafi
Mali

Shugaban Sojan Mali Sanogo ya musanta sake wani juyin mulki

Shugaban sabuwar gwamnatin mulkin sojan kasar Mali Capt Amadou Sanogo, ya fito ta kafofin yada labarai yana musanta cewa an hallaka shi cikin wani sabon juyin mulkin.

Reuters/Malin Palm
Talla

Ya bayyana cewa kofa a bude ta ke wajen tattaunawa da ‘yan tawayen Azbinawa, kuma za a gudanar da zaben demokaradiya da zaran lamuran tsaro sun daidaita a cikin kasar.

Ranar Laraba da ta kananan habsoshin soja suka kifar da gwamnati Amadou Toumani Toure, ana gab da gudanar da zabe cikin watan gobe, inda suka zargi gwamnati da rashin samar da kayan aiki wa sojojin dake tunkarar ‘yan tawayen Azbinawa na arewaci. Har yanzu babu cikekken bayanin inda hambararren shugaba Toure ya ke bayan wannan juyin mulki.

Shaguna da gidajen mai sun ci gaba da kasancewa a rufe, inda mutane ke zargi sojoji da wasoson dukiyar mutane. Tuni sabbin mahukuntan sojan kasar suka nemi sojoji su mutunta tsarin bin doka da oda.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.