Isa ga babban shafi
Wasanni

Anya Manchester City za ta kamo Liverpool kuwa?

Liverpool ta kama hanyar lashe kofin gasar firimiyar Ingila karo na farko cikin shekaru 30 bayan ta lallasa mai rike da gambin gasar wato Manchester City da kwallaye 3-1 a Anfield. Pep Guardiola ya ce, bai sani ba ko za su iya kulle tazarar da Liverpool ta ba su a teburi.

Lokacin da Mohamed Salah ya ci kwallo ta biyu a fafatawarsu da Manchester City a Anfield
Lokacin da Mohamed Salah ya ci kwallo ta biyu a fafatawarsu da Manchester City a Anfield Carl Recine/Reuters
Talla

Yanzu haka Liverpool na jan ragamar teburin da maki 34, inda ta bai wa Manchester City tazarar maki 9.

Liverpool ta jefa kwallaye biyu cikin ragar City a cikin mintina 13 na farko ta hannun Fabinho da Mohamed Salah, kafin Sadio Mane ya kara ta uku bayan dawowa daga hutun rabin lokaci.

A karo na uku kenan da Manchester City ke shan kashi a wasanni takwas na gasar firimiyar Ingila a bana, abin da ke nuna cewa, akwai gagarmin aiki a gabanta muddin tana son kare wannan kambi da ke hannunta.

Kodayake ya yi wuri a tsayar da hasashe kan kungiyar da za ta lashe gasar ta bana, lura da cewa, akwai sauran wasanni da dama da za a yi nan gaba.

Watakila saboda haka ne, kocin Liverpool, Jurgen Kloop ya bayyana cewa, akwai sauran aiki a gabansu duk da cewa, sun bai wa Manchester City tazarar maki 9.

A cewar kocin, jan ragamar teburin gasar a cikin watan Mayun badi, ita ce mafi muhimmanci amma ba a cikin wannan wata na Nuwamba ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.