Isa ga babban shafi
Wasanni

Tottenham za ta ci gaba da matsin lamba ga Chelsea

Mai horar da tawagar kwallon kafa ta Tottenham Mauricio Pochettino ya bayyana cewa, babu wani abu da zai gagari kungiyar a kokarinta na ci gaba da matsin lamba ga Chelsea da ke jagorantar teburin gasar Premier a Ingila.

'Yan wasan Tottenham Hotspurs na ci gaba da kokarin rage tazarar maki da ke tsakaninsu da Chelsea mai jan ragamar teburin gasar Premier a Ingila
'Yan wasan Tottenham Hotspurs na ci gaba da kokarin rage tazarar maki da ke tsakaninsu da Chelsea mai jan ragamar teburin gasar Premier a Ingila Reuters / Andrew Couldridge Livepic
Talla

A gobe Laraba ne Tottenham da ke a matsayi na biyu a taburin Premier za ta ziyarci Swansea City don fafatawa, yayin da ta kara samun kwarin gwiwar yiwuwar lashe kofi a bana bayan Chelsea ta sha kashi a hannun Crystal Palace da ci 2-1 a makon jiya, abin da ya rage tazarar makin da ke tsakaninta da Totenham.

Sannan kuma Tottenham ta samu nasara a fafatawar da ta yi da Burnley da ci 2-0, lamarin da ya sa a yanzu aka samu tazarar maki 7 a tsakanisu sabanin 10 da ke tsakaninsu a baya.

Ana ganin cewa akwai yiwuwar wannan tazarar ta sake raguwa a gobe Laraba, musamman idan Chelsea ta yi rashin nasara a hannun Manchester City a karawar da su ma za su yi a goben.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.