Isa ga babban shafi
Wasanni

Kamaru ta yi waje da Ghana a gasar Afrika

Tawagar kwallon kafa ta Kamaru ta fitar da Ghana daga gasar cin kofin nahiyar Afrika da ake gudanarwa a Gabon bayan sun tashi wasa da ci 2-0 a fafatawarsu ta jiya a birnin Franceville.

Michael Ngadeu-Ngadjui da ya zura wa Kamaru kwallon farko a karawarsu da Ghana
Michael Ngadeu-Ngadjui da ya zura wa Kamaru kwallon farko a karawarsu da Ghana RFI/Pierre René-Worms
Talla

Kamaru ta samu nasarar zura kwallayen ne bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, in da Michael Ngadeu-Ngadjui ya zura kwallon farko a minti na 72, yayin da Christian Bassogog ya zura ta biyu a minti na 93.

A ranar Lahadi mai zuwa ne Kamaru za ta kara da Masar a matakin wasan karshe na wannan gasar ta cin kofin Afrika wadda ita ce, karo na 31.

Kocin Kamaru Hugo Broos ya ce, burinsu na zuwa matakin wasan karshe ya cika duk da cewa, Ghana ta fi su kwarewa wajen murza tamaula.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.