Isa ga babban shafi
Tattalin arziki

Arzikin kasashen Kudu da Sahara zai habbaka-IMF

Hukumar Bada Lamuni ta Duniya ta ce, tattalin arzikin kasashen da ke Kudu da Sahara zai samu habakar da ya kai kusan kashi 3 da rabi a cikin wannan shekara, sabanin kusan kashi 3 da aka samu a  bara, sai dai akasarin kasashen na fama da matsalar bashin da ke musu tarnaki.

Shugabar Asusun Bada Lamuni na Duniya, Christine Lagarde
Shugabar Asusun Bada Lamuni na Duniya, Christine Lagarde REUTERS/Denis Balibouse
Talla

Rahotan da hukumar  ta fitar ya bayyana kasashen da tattalin arzikinsu ke samun tagomashi da suka hada da Jamhuriyar Benin da Burkina Faso da Habasha da Ghana da Cote d’Ivoire da Rwanda da Senegal da kuma Tanzania.

Rahotan ya ce, wadannan kasashen sun samu habakar da ta kai sama da kashi 6 a shekarar 2017, kuma akwai kyakyawar fatar da ke nuna cewar zai zarce haka a bana.

Hukumar ta ce, kasar Habasha ita ta yi zarra wajen samun habakar wanda alkaluma suka nuna cewar ya zarce kashi 10.

Abebe Aemro Selassie, daraktan hukumar dake kula da Afrika ya ce, kananan 'yan kasuwa a wadanann kasashe na samun ci gaba a harkokinsu na yau da kullum, yayin da kasashe 15 daga yankin ke fama da bashi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.