A ranar daya ga watan Octoba ne, Najeriya za ta yi bukin cika shekaru 52 da samun ‘Yancin kai daga Turawan mulkin mallaka. Amma Wasu na cewa har yanzu tana da sauran tafiya, idan aka kwatanta kasar da sauran kasashen da suka samu ‘Yancin kai tare. A cikin Shirin Duniyarmu A Yau, Bashir Ibrahim Idris ya yi nazari game da matsalolin Najeriya tare wasu tsoffin shugabanin kasar.