Isa ga babban shafi
Isra'ila

UNICEF ta gargadi Isra’ila akan keta hakkin kananan yara

Hukumar Majalisar Dukin Duniya ta UNICEF ta gargadi hukumomin kasar Isra’ila da sun dinga kare hakkin yara Falasdinu dake a tsare a gidan yarin kasar. Wanan na zuwa ne bayan da wani bicinke da hukumar UNICEF ta gudanar da ya nuna cewar Isra’ila na keta hakkin yara yan kasar Falasdinu da ‘Yan sanda Isra’ila suka kama.  

Wasu kananan yara
Wasu kananan yara UNICEF/NYHQ2011-1134/Kate Holt/Rumania/2011
Talla

Daga cikin abubuwan dake cima UNICEF tuwo a kwarya kamar yadda rahotanni suka nuna shine yadda Isra’ila ke tisa keyar yaran kanana gabban kotun sojin domin fuskantar Shari’a, dama yadda ake kama wadannan nyara akan zargi cewar suna da alaka da ‘Yan kungiyoyin dake ta da zaune tsaye a yankin.

A yanzu haka bnicike na nuna cewar yaran yan kasar Falesdinu da shekaru na su bai wuce 13 zuwa 14 ba na fuskantar daurin zaman gidan yari na watani shida zuwa shekaru 10.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.