Bordeaux ta fusata da hukuncin hukumar kwallon kafar Faransa
Hukuncin hukumar kwallon kafar Faransa na bai wa Bordeaux rashin nasara a wasansu da Rodez da aka dakatar ya hana kungiyar samun damar tsallakewa daga gasar Lig 2.
Wallafawa ranar:
Yayin wasa tsakanin kungiyoyin biyu ne a ranar 2 ga watan Yuni wani magoyi baya da ya kutso cikin fili ya hankade Lucas Buades na Rodez dalilin da ya tilasta dakatar da wasan.
Wannan dalili ne ya sanya baiwa Bordeaux rashin nasara a karawar Wanda ke nuna cewa ta kammala gasar a matsayin ta 2 yayinda ita kuma Rodez ta tsallake rukunin ‘yan dagaaji na teburin gasar ta Lig 2, ta biyu mafi girma a Faransa.
Tuni dai Bordeaux ta fusata da wannan hukuncin inda ta sha alwashin daukaka kara ga kwamitin koli na harkokin wasanni a kasar don bi mata hakki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu