Bayern ta dakatar da Mane saboda naushin da ya kirɓa wa Sane
Kungiyar Bayern Munich ta dakatar da dan wasanta Sadio Mane daga buga wasa daya, sakamakon naushin da ya kirba wa abokin wasansa Leroy Sane, bayan rashin jituwar da ta shiga tsakaninsu.
Wallafawa ranar:
Wannan mataki dai na nufin Sadio Mane, mai shekaru 31, ba zai kasance cikin tawagar kungiyarsa da za ta fafata wasa da Hoffenheim ba a ranar Asabar mai zuwa.
Baya ga dakatarwar wasa guda Mane zai kuma biya tarar kudaden da a bayyana adadinsu ba.
Babu dai wanda zai iya tabbatar da hakikanin abinda ya haifar da takadddama tsakanin ‘yan wasan na Bayern Munich, illa wasu majiyoyi da suka ruaito cewar Mane ya zargi Leroy Sane da raina shi, abinda ya sa suka fara musayar yawu tun a cikin filin wasan da Manchester City ta lallasa su da kwallaye 3-0 a ranar Talata.
Bayan shiga dakin hutu da adana kaya ne kuma lamarin ya kai ga bai wa hammata iska a tsakanin ‘yan wasan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu