Isa ga babban shafi

Madrid na shirin karbar bakuncin Chelsea a gasar Turai

Yau za’a fafata tsakanin kungiyar Real Madrid da Chelsea a gasar cin kofin zakarun nahiyar Turai, inda ake saran kungiya daya daga cikin su ta samu damar wucewa zuwa zagaye na gaba.

Karim Benzema (Real Madrid) da N'Golo Kanté (Chelsea),
Karim Benzema (Real Madrid) da N'Golo Kanté (Chelsea), © JAVIER SORIANO / AFP
Talla

A karawar da akayi makon jiya, Madrid ta doke Chelsea mai rike da kofin gasar da ci 3-1 a wasan da ya gudana a Ingila wanda Karim Benzema ya jefa kwallayen guda 3 shi kadai.

Karim Benzema,Dan wasan real madrid
Karim Benzema,Dan wasan real madrid REUTERS - SUSANA VERA

Wannan ya sa ake kallon karawar ta yau a matsayin mai matukar muhimmanci ga kungiyoyin guda 2, kuma dole daya daga cikin su ta fice daren yau.

Rahotanni sun ce Chelsea wadda ta lallasa Southampton da ci 6-0 a gasar Firimiya ba zata samu damar amfani da yan wasan ta irin su Romelu Lukaku da Callum Hudson-Odoi da Ben Chilwell ba saboda raunukan da suka fama da shi.

Romelu Lukaku
Romelu Lukaku Action Images via Reuters - JOHN SIBLEY

Mai horar da Yan wasan Madrid Carlo Ancelotti yace har yanzu da sauran aiki a gaban su kafin samun tikitin wasan kusa da na karshe a karawar yammacin yau.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.