Isa ga babban shafi
Najeriya - Senegal

Buhari ya taya Senegal murnar lashe kofin Afirka

Shugaban Najeriya Muhammadu ya taya kasar Senegal murnar nasarar da ta samu a gasar cin kofin Afrika da aka kammala a Kamaru.

Dan wasan Senegal da Liverpool Sadio Mané dauke da kofin da suka lashe a gasar AFCON da Kamaru da karbi bakwanci 2022.
Dan wasan Senegal da Liverpool Sadio Mané dauke da kofin da suka lashe a gasar AFCON da Kamaru da karbi bakwanci 2022. CHARLY TRIBALLEAU AFP
Talla

Buhari ya mika sakon ne lokacin da ya karbi bakuncin Jakadan kasar Senegal a Najeriya, Babacar Ndiaye, a wani taron bankwana da aka yi a fadar gwamnati da ke Abuja jiya Alhamis, inda ya roke shi da ya mika sakon taya murna ga Shugaba Macky Sall kan nasarar da Teranga Lions suka samu a AFCON.

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Femi Adesina ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar jiya Alhamis mai taken, ‘Shugaba Buhari ya yi bankwana da jakadan Senegal, ya kuma taya kasar murnar nasarar da ta samu a AFCON.

Buhari ya kuma yi wa jakadan mai barin gado fatan samun nasara a duk inda zai yi aiki a gaba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.