Isa ga babban shafi
Wasanni - Kamaru

Kamaru: Mutane 8 sun mutu 50 sun jikkata dalilin turmutsitsi a filin wasa

Mutane 8 sun mutu yayin da wasu 50 suka jikkata a Kamaru, sakamakon turmutsitsi mutanen da ya auku a wajen filin wasan kwallon kafa na kasar da ke birnin Yaounde.

Hoton da aka dauka daga faifan bidiyon da ya nuna harabar filin wasan kwallon kafa na Olemebe da aka samu turmutsitsi a birnin Yaounde da ke kasar Kamaru. 24 ga Janairu, 2022.
Hoton da aka dauka daga faifan bidiyon da ya nuna harabar filin wasan kwallon kafa na Olemebe da aka samu turmutsitsi a birnin Yaounde da ke kasar Kamaru. 24 ga Janairu, 2022. © France 24 screengrab
Talla

Lamarin ya auku ne, a lokacin da cincinrindon jama’a suka yi yunkurin shiga filin ta wasan na Olembe da ke babban birnin kasar domin kallon wasan da Kamaru za ta kara da Comoros, wanda daga karshe mai masaukin bakin ta samu nasara 2-1.

Ma’aikatar lafiyar Kamaru ta ce, cikin mutanen 8 da suka mutu a turereniyar akwai  mata biyu ‘yan shekara talatin, maza hudu suma da shekarunsu suka kai tallatin talatin, sai yaro daya, da kuma wani mutum da iyalansa suka tafi da gawarsa.

Ma'aikatar ta kara da cewa, cikin mutane 50 da suka jikkata,  akwai wani jariri da aka tattake yayin turmutsitsi, sai dai an yi nasarar ceto ransa jaririn, tare da garzayawa da shi babban asibitin birnin Yaounde.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.