Isa ga babban shafi
Wasanni - Kamaru

'Yan bindiga sun yi wa 'yan jarida uku fashi a Kamaru yayin gasar AFCON

‘Yan bindiga da sun yi wa wasu ‘yan jarida uku daga kasar Algeria fashi, tare da yin amfani da wuka wajen jikkata su a daren ranar Lahadi.

Wata kasuwar sayar da ababen bushe bushe na Vuvuzela a birnin Younde na Kamaru a ranar 7 ga watan Janairun 2022.
Wata kasuwar sayar da ababen bushe bushe na Vuvuzela a birnin Younde na Kamaru a ranar 7 ga watan Janairun 2022. AFP - KENZO TRIBOUILLARD
Talla

Kamfanin dillancin labaran kasar Algeria na APS ya ruwaito cewar, ‘yan jaridar da ke aikin daukar labaran gasar cin kofin kasashen Afrika a Kamaru, sun gamu da tashin hankalin ne, a yayin da suke barin dakunan otal dinsu da ke birnin Douala.

Baya ga jikkata ‘yan jaridar da suka yi, ‘yan bindigar sun yi awon gaba da jakar kudaden ‘yan Algerian, da wayoyi da kuma Komfutocinsu.

A halin da ake ciki hukumar kwallon kafar Afirka CAF ta ta hada gwiwa da jami’an tsaro wajen gudanar da binicke akan lamarin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.