Kungiyoyin Firimiya sun hana bakin 'yan wasa zuwa kasashensu saboda Korona
Hukumar gasar Firimiyar Ingila ta sanar da cewa kungiyoyin ta ba za su kyale 'yan wasansu halartar wasannin neman cancantar shiga gasar cin kofin duniya da kasashensu za su buga ba a watan gobe.
Wallafawa ranar:
Matakin dai ya shafi ‘yan wasan da kasashensu ke cikin wadanda Birtaniya ta bayyana a matsayin masu hatsari saboda fama da annobar Korona.
Jim kadan bayan sanarwar Firimiya ne kuma, gasar La Liga ta Spain ta ce za ta goyi bayan kungiyoyin da suka yanke shawarar kin sakin 'yan wasa zuwa kasashen da aka sanya cikin jerin masu hatsari saboda Korona, la’akari da cewa 'yan wasan da suka yi balaguro zuwa kasashen masu fama da cutar ta Korona, dole ne su bi ka'idojin kebe kansu bayan komawa Turai matakin da ka iya sanya ‘yan wasan rasa samun bugawa kungiyoyin nasu wasanni.
A halin yanzu wannan mataki na nufin kungiyoyi irinsu Liverpool ba za ta saki taurarinta da suka hada da Mohamed Salah ba, da Fabinho, Roberto Firmino da kuma Alisson Becker don wasannin neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya na Brazil da kuma Masar.
Kamar 'yan wasan Liverpool uku, taurarin Manchester City Ederson da Gabriel Jesus ma ba za su samu damar bugawa Brazil wasannin neman cancantar ba.
A takaice dai a Firimiya Lig kadai, kusan ‘yan wasa 60 ba za su samu damar zuwa kasashensu don haska musu a wasannin sharar fagen gasar cin kofin duniya da za su yi ba a wata mai kamawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu