Isa ga babban shafi
Wasanni - Kwallon Kafa

Gasar Euro 2020: Rana ba ta karya

A wannan Juma’ar ake fara gasar cin kofin kasashen Turai da ake kira Euro 2020 wanda annobar korona ta hana gudanar da shi bara.

Kofin gasar kasashen nahiyar Turai ta Euro 2020.
Kofin gasar kasashen nahiyar Turai ta Euro 2020. Fabio FRUSTACI ANSA/AFP/File
Talla

Gasar wadda tsohon shugaban hukumar kwallon kafar Turai Michel Platini ya bayyana za’a dinga zagayawa da ita tsakanin kasashen dake yankin a wannan karo za’a gudanar da ita ne a gaban takaitattun yan kallo  saboda dokokin kula da lafiya.

A wasan farko na gasar za’a kara ne tsakanin kasar Italia da Turkiya a filin wasan Stadio Olimpico dake birnin Rome.

Kasar Faransa ke sahun gaba cikin jerin kasashen da ake saran su lashe gasar saboda fitattun Yan wasan da take da su da yanzu haka suke tashe a duniya.

Jaridar L’Equipe ta kasar a sharhin da tayi kan gasar ta wallafa hotunan fitattun Yan wasan Faransa da suka hada da Kylian Mbappe da Karim Benzema da Antoine Griezmann inda tace kowacce kasa a Turai ta mayar da hankali akan su.

'Yan wasan Faransa Karim Benzema yayin atsaye tare da Kylian Mbappe.
'Yan wasan Faransa Karim Benzema yayin atsaye tare da Kylian Mbappe. © AFP

Wasu daga cikin Yan wasan da Faransa ta lashe kofin duniya ke tinkaho da su sun hada da N’Golo Kante da Sisoko da Fekir da Olivier Giroud da makamantan su.

Hankalin mutane zai karkata kan rawar da Karim Benzema zai taka bayan dawo da shi cikin tawagar Yan wasan Faransa sakamakon dakatarwar da aka masa tun daga shekarar 2015.

Cristiano Ronaldo yayin atsaye tare da takwarorinsa na tawagar kwallon kafar kasar Portugal.
Cristiano Ronaldo yayin atsaye tare da takwarorinsa na tawagar kwallon kafar kasar Portugal. © Shutterstock

Kasar Portugal mai rike da kofin har yanzu tana kan ganiyar ta da zaratan 'yan wasa irinsu Cristiano Ronaldo wanda ake saran ya jagorancin kasar wajen kare kambin da suka ci a gasar da ta gabata.

'Yan wasan tawagar kwallon kafar kasar Belgium.
'Yan wasan tawagar kwallon kafar kasar Belgium. © AFP

Kasar Belgium wadda yanzu haka ke matsayi na farko a matakin FIFA cikin jerin kasashen da suka fi kowa tagomashi a duniya na da zaratan Yan awasa irin su Kevin de Bruyne da Romanu Lukaku da Eden Hazard da ake saran su cirewa kasar kitse a wuta.

'Yan wasan tawagar kwallon kafar kasar Ingila
'Yan wasan tawagar kwallon kafar kasar Ingila © The FA via Getty Images

Ita kuwa Ingila na dauke ne da tawagar Yan wasa matasa masu jini a jika wadanda ke neman suna a karkashin manajan su Gareth Southgate, yayin da Jamus ke kokarin farfadowa bayan rashin nasarorin da ta samu a shekarun baya.

Za’a kwashe makwanni ana fafatawa tsakanin kasashen dake wannan nahiyar, yayin da ake saran samun sabbin fitattun Yan wasan da za suyi suna domin samun kwangiloli masu tsoka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.