Mbappe zai ci gaba da zama a PSG - Al-Khelaifi
Shugaban kungiyar Paris Saint - Germain na kasar Faransa Nasser Al-Khelaifi ya kawo karshen duk wasu zantuka dake alakanta batun sayar da gwarzon dan wasan gaba na kungiyar Kylian Mbappe.
Wallafawa ranar:
Da yake shaidawa jaridar L’Equipe, Al-Khalifi yace, Mbappe zai ci gaba da kasancewa daram a babban birnin Faransa wata Paris, yana mai cewa, basu da niyyar sayar da Mbappe, hasalima dan wasan bazai koma ko ‘ina a kyauta ba.
A watan Yuni shekarar 2022 ya kamata kwantiragin Mbappe ya kare, kuma ansha alankata shi da komawa kungiyar Real Madrid dake Spain.
Barcelona bata kudin sayen Neymar
Shugaban na PSG yayi kuma tsokaci dangane da batun komawar Neymar Junior zuwa Barcelona, inda yace kungiyar ta Katolonia bata da kudin sayen dan wasan a yanzu, hasalima dan wasan bashi da niyyar yiwa tsohowar kungiyarsa kome.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu