An sake lallasa Liverpool a gasar Firimiya
Alamu na kara tabbata kan cewa ba lallai bane kungiyar Liverpool ta kwashi wani abin azo a gani kakar wasa ta bana a gasar Premier League, bayan kayen da ta sha da 1-0 a hannun Fulham yayin fafatawarsu a ranar Lahadi.
Wallafawa ranar:
Karo na 6 kenan da Liverpool ke shan kaye a jere a wasannin da ta buga a baya bayan nan.
Wani karin koma baya ga masu rike da kofin gasar Firimiyar, shi ne idan Chelsea dake mataki na hudu ta samu nasarar doke Everton a wasan da za su buga a yau. Muddin Chelsea ta lashe wasan nata, za ta kara tazarar da ta baiwa Liverpool zuwa maki 7 sabanin 4 dake tsakaninsu a yanzu haka.
Rabon da Liverpool ta nuna karsasshi a wasanninta tun gaf da bikin ranar Kirsimeti a karshen shekarar 2020, kalubalen da ake dangantawa da jinyar raunukan da wasu fitattun ‘yan wasan kungiyar ke yi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu